Shugaban kungiyar malamai na jiha, Comrade Abdulkadir Yunusa Jigawa ya sanar da hakan ta cikin shirin Radio Jigawa na mako mako mai suna Fitila
Yace hakan na daga cikin kudirin gwamnatin jihar Jigawa na cike gurbin
malaman makaranta da suka yi ritaya da kuma daukar kwararrun malamai aikin
koyarwa.
Comrade Abdulkadir Yunusa Jigawa ya kara da cewar gwamna Muhammad Badaru
ya bada tabbacin mayarda malaman j-teach 400 zuwa 800 zuwa cikakkun malamai na
dindindin
Ya kara da cewar malaman makaranta dari tara ne suka yi ritaya a jihar
Jigawa daga watan janairu zuwa watan da muke ciki.
Comrade Abdulkadir Jigawa yana mai cewar gwamnatin jiha da sauran
hukumomin bada tallafi na duniya sun bullo da matakai na kara inganta alamurran
ilmi.
Yace kungiyar malamai ta Jigawa ta gamsu da yadda gwamnati ke kula da
harkokin ilmi, musamman a bangaren gine gine da samarda kayayyakin koyo da
koyarwa da kuma yiwa malamai Karin girma.
Comrade abdulkadir Jigawa yace a nata bangaren kungiyar zata raba dashen
Darbejiya dubu daya domin dasawa a makarantu da nufin samar da mahalli mai kyau
a makarantu
Jigawa State Radio –
Facebook Page